bayyinaat

Published time: 25 ,January ,2017      12:22:08
Idan kuwa kuka same shi yana kamewa daga haram to (har yanzu dai) ku yi a hankali kada ya rude ku, domin lallai sha'awowin halittu suna sassabawa, sau da yawa wani wanda yake nisantar dukiyar haram komai yawanta, (amma) kuma (da zai samu dama, da) ya dora kansa (ya hau) kan wata mummunar mata mai muni (duk muninta) sai ya aikata haram (na zina) tare da ita.
Lambar Labari: 23

Da Sunan Allah Madaukaki
Godiya ta tabbata ga Allah (s.w.t)
Aminci ya k'ara tabbata ga bayinsa wad'anda ya zab'a
"Kawai Allah yana son ya tafiyar da dauda daga gareku ne Ahlul Baiti kuma ya tsarkake ku tsarkakewa " .
"Lallai ni mai bar muku nauyaya biyu ne; Littafin Allah da Ahlin gidana, ba zaku tab'a b'ata ba bayana har abada matuk'ar kun yi rik'o da su " .
Kuma sama ya d'aukaka ta, kuma ya sanya sikeli. Kuma ku daidaita awo da adalci, kada ku rage sikelin. Kuma k'asa ya sanya ta domin talikai ne .

Kamalar dan Adam wani abu ne mai wahalar isa zuwa gareshi domin hanyoyin suna da surkukiya mai wahalar gaske, sai dai akwai ma'aunai da suke nuna cewa mutum yana samun ci gaba. Wadannan ma'aunan suna iya kasancewa na tunani ko na aiki, ta yadda kyawawan halayen mutum su ne suke iya nuna cewa shi salihi ne ko fasidi ba yawan ibadojinsa ba, sau da yawa wani yake bauta amma babu inda take zuwa, imma dai don bai riki imamin zamaninsa ba, ko ya riki masoya Allah makiya, ko halayensa sun munana, don haka a cikin kyawawan halaye ne masu rige zasu yi rige domin kai wa ga kamala.
A cikin littafin alKafi na sheikh Kulaini ya zo daga gareshi daga Usman dan Isa, daga Ishak dan Ammar da waninsu, daga Abu Abdullah Imam Ja'afar Sadik (a.s) ya ce: Kada ku rudu da sallarsu, ko da azuminsu, domin sau da yawa ta yiwu mutum ya riki yin salla da azumi ta yadda da ya bar su sai ya samu jin babu dadi, amma ku jarraba su gun gaskiyar magana, da bayar da amana .
A wata ruwayar Imam Ja'afar Sadik yana cewa ne: Duk wanda harshensa ya gaskata, to aikinsa zai tsarkaka .
 Lamarin kiyaye hakkin mutane ya kai ga hatta cikin abin da ya shafi mutum ya hau kansa ya kiyaye hakkin mutane a cikinsa. Lamarin ya kai ga manzon Allah (s.a.w) yana la'anar mai cin guzurinsa (a tafiya) shi kadai ya bar sauran mutane.
Jarabawar da take gaban mutum tana da girma da wahala matuka, kuma kowacce ana son ya kiyaye cikinta don ya kasance mutum mai kamala wurin Allah madaukaki. Muna iya duba wannan ruwaya don muga santsin wannan hanya kamar haka:
Daga littafin Ihtijaj na Dabarasi, Mansur Ahmad dan Abi Dalib Addabrasi , da sanadinsa zuwa Imam Hasan al'Askari (a.s) daga Imam Ridha (a.s) ya ce: Aliyyu dan Husain (a.s) ya ce: 
(Yaudara da nuna Salihanci) Idan kuka ga mutum yanayinsa da basirarsa sun kyautata, yana kaikaice maganarsa, da nuna kaskantar da motsinsa, to ku yi a hankali kada ya rude ku, sau da yawa a kan samu wanda samun duniya da hawa kan haram yake yi masa wahala saboda raunin niyyarsa, da wulakantuwarsa da tsoron zuciyarsa, sai ya nuna addini a matsayin tarkonsa, shi ba ya gushewa yana yaudarar mutane da zahirinsa, idan kuma ya samu damar aikata yin haram sai ya fada masa.
(Dukiya da Mata) Idan kuwa kuka same shi yana kamewa daga haram to (har yanzu dai) ku yi a hankali kada ya rude ku, domin lallai sha'awowin halittu suna sassabawa, sau da yawa wani wanda yake nisantar dukiyar haram komai yawanta, (amma) kuma (da zai samu dama, da) ya dora kansa (ya hau) kan wata mummunar mata mai muni (duk muninta) sai ya aikata haram (na zina) tare da ita. 
(Samuwar Hankali) Idan kuwa kuka same shi yana kamewa daga wannan (zina) to (har yanzu dai) ku yi hankali da shi kada ya yaudare ku har sai kun duba hankalinsa, sau da yawa wani ya bar wannan duka amma ba shi da wani hankali mai karfi, sai ya kasance abin da yake batawa da jahilcinsa ya fi abin da yake gyarawa da hankalinsa.
(Son Zuciya) Amma idan kuka sami hankalinsa mai karfi ne, to (har yanzu dai ku yi hattara da shi) ku yi hattara dai kada ya yaudare ku har sai kun ga shin yana tare da son ransa a kan (watsi da) hankalinsa, ko kuma yana tare da hankalinsa ne a kan (watsi da) son ransa.
(Son Shugabanci Batacce) Sannan yaya sonsa yake ga shugabanci na barna da nisantarsa gareshi. Hakika a cikin mutane akwai wanda ya rasa duniya da lahira, yana barin duniya don duniya, yana ganin dadin jagorancin barna ya fi dadin dukiyoyi da ni'imar halal da aka halatta, sai ya bar wannan duka don neman jagoranci har sai idan aka gaya masa cewa ka ji tsoron Allah, sai girman kai ya kwashe shi da barna, to wutar jahannama ta wadatar masa, kuma tir da makoma .
Yana mai gangara kawararo gaba gadi, farkon barna tana jansa zuwa ga mafi nisan matukar tabewa, kuma ubangijinsa yana mai barinsa da kansa bayan nemansa ga abin da ba zai iya masa ba a cikin taurin kansa, shi yana mai halatta abin da Allah ya haramta, yana mai haramta abin da Allah ya halatta, ba ruwansa da abin da ya kubuce masa na addininsa idan dai shugabancin da ya tabe saboda shi ya kubuta, wadannan su ne wadanda Allah ya yi fushi da su ya la'ance su kuma ya tanadar musu da azaba mai wulakanci .
(Mutumin Kwarai) Sai dai cikakken mutum, madalla da mutumin da yake sanya son ransa kan biyayya ga umarnin Allah madaukaki, kuma karfinsa ya kasance ya bayar da shi cikin yardar Allah, yana ganin kaskanci tare da gaskiya shi ya fi kusanci zuwa ga daukakar har abada a kan daukaka cikin barna.
Kuma ya san cewa mafi karancin abin da zai iya jurewa na cutuwarta (duniya) zai kai shi ga dawwamar ni'ima ne a gidan da ba ya rasuwa ba ya karewa(lahira), kuma mafi yawan abin da yake samun sa na farin cikinta (duniya) idan ya bi son ransa zai kai shi ga azabar da babu yankewa gareshi babu gushewa (a lahira), to wannan mutumin madalla da shi (ya cika) mutum, da shi ne zaku yi riko, kuma ku yi koyi da sunnarsa (aikinsa), kuma ku yi tawassali da shi zuwa ga ubangijinku, domin shi ba a mayar masa da addu'a, kuma ba a hana shi abin da ya nema.
Littafin da yake gabanka mai karatu shi ne Littafin "Sakon Hakkoki" na Imam Aliyyu Zainul-abidin wanda aka san shi da asSajjad, ko "Sayyidus Sajidin". Shi bayani ne mai kima matuka da ya ishi mutun rayuwar duniya gaba daya, wanda da al'umma ta kiyaye shi, da ba a samu sabani tsakanin mutane biyu ba, da duniya ta koma kamar aljanna saboda zaman lafiya, da yalwa da arziki, da kauna da so sun maye gurbin kiyayya da gaba, da sulhu da zaman lafiya sun maye gurbin yaki da kashe-kashe!.
Imam Ali asSajjad shi ne Imami na Hudu cikin jerin wasiyyan annabi (s.a.w) wadanda su ne ruwayoyi suka ambace su da Ahlul-baiti da suka hada sayyida Zahara (s.a) da kuma goma sha biyu tsarkaka da manzon Allah (s.a.w) ya yi umarni da riko da su bayan wafatinsa kamar yadda ya zo a manyan littattafan ruwayoyi na hadisai. Sai dai kauce wa wannan wasiyya ta manzon Allah (s.a.w) ya sanya al'umma fadawa cikin rudani da bambance-bambance har zuwa wannan zamanin.
Allah (s.w.t) yana fada cewa: "Kawai Allah yana son ya tafiyar da daud'a daga gareku ne Ahlul-baiti kuma ya tsarkake ku tsarkakewa" .
Wasiyyar manzon Allah (s.a.w) ga al'ummarsa: "Lallai ni mai bar muku nauyayan (alkawura) biyu ne; Littafin Allah da Ahlin gidana, ba zaku taba bata ba bayana har abada matukar kun yi riko da su" .
Hadisai sun yi nuni da su a littattafai daban-daban, kamar yadda Shehu Usman dan Fodio Allah ya kara masa yarda ya kawo sunansu a cikin Nasihatu Ahluzzaman a yayin da yake kawo salsalar Imam Mahadi (a.s) wanda zai zo a karshen duniya. Da al'umma ta fuskanci koyarwarsu da ba ta samu kanta cikin wannan faganniya da rudani ba, sai dai abin da ya faru ya riga ya wakana.
Domin tubarraki zamu so kawo sunyensu kamar haka: Imam sayyidi Ali (a.s), sai Imam Hasan (a.s), sai Imam Husain (a.s), sai Imam Aliyyu Zainul-abidin (a.s) wanda shiryarwarsa take kunshe cikin wannan littafin, sai Imam Muhammad al'Bakir (a.s), sai Imam Ja'afar asSadik (a.s), sai Imam Musa alKazim (a.s), sai Imam Ali arRidha (a.s), sai Imam Muhammad al'Jawad (a.s), sai Imam Ali al'Hadi (a.s), sai Imam Hasan al'Askari (a.s), sai Imam Muhammad al'Mahadi (a.s).
Da yake ruwayoyi biyu ne, don haka mun kawo su da maimaicin da suka zo da shi a ruwayoyi mabambanta saboda sabanin da yake tsakaninsu, sai dai mun sanya ruwayar da tafi fa'idoji masu yawa, ita kuwa ruwayar da ta fi sanadi mai karfi mun sanya ta a kasa.
Muna rokon Allah ya sanya Imam Khoamain (k.s) cikin ladan wannan rubutun sakamakon yau ta yi daidai da ranar juyayin wafatinsa.

Imam Aliyyu Zainul-abidin (a.s)
Tarjamar: Hafiz Muhammad Sa'id
Haidar Center for Islamic Propagation
+234 803 215 6884 (Text only or (Line, Tango, Viber, Whatsapp, Telegram)
(hfazah@yahoo.com) (hfazah@hotmail.com)
Saturday, June 04, 2011

comments Masu kallo
Suna:
Adireshin Email:
* ra'ayi: