bayyinaat

Kurani
Tarihin Kurani
Sabida irin wannan munanan ayyuka Allah (SW) ya saukar da ayar la'ana ga Abu Lahab har zuwa ranar qiyama
Karanta Kur'ani da Koyonsa
Daga Muhammad dan Fudail daga Abul Hasan (a.s) ya ce: "Na tambaye shi: ina karanta Kur'ani sai fitsari ya kama ni sai in tashi in yi fitsari sannan in yi tsarki in wanke hannuna sannan sai in koma wa littafi sai in karanta shi? Sai ya ce: A'a, har sai ka yi alwalar salla". Daga littafin Hisal da sanadinsa daga Ali dan Abu Dalib (a.s) a wani hadisi guda dari hudu ya ce: bawa ba ya karanta Kur'ani idan ya kasance ba bisa tsarki ba har sai ya yi tsarki" .
Kur’ani da mutum
Bayan wafatin manzon tsira imam Ali (a.s) wanda shi ne ya fi kowane mutum sanin kur’ani bayan manzon rahama, ya zauna a gidansa bai wuce wata shida ba da wafatin manzon Allah (s.a.w) sai da imam Ali (a.s) ya hada kur’ani gaba dayansa a bisa jerin yadda ya sauka gaba daya, aya tana bin aya, sura tana bin sura .
Mene ne kur’ani
Kur’ani a lugga yana nufin karatu, Allah (s.w.t) yana cewa; “Idan muka karanta shi sai ka bi karatunsa”. Kur’ani; shi zance ne kuma littafi na Allah mai gajiyarwa ga wani ya zo da shi da Allah ya saukar da shi wahayi ga annabi (s.a.w) ta hannun Jibril (a.s) wanda aka rubuta a littafin mus’haf, da ya tabbata ta hanyar labarai mutawatirai wadanda ba yadda za a yi su zama karya, wanda kuma aka sanya karanta shi bauta ne ga Allah”.