Jagorancin Al'umma

Jagorancin Al'umma

Bayan yin bayanin wadannan nazarorin, ya dace mu bayar da amsar wannan tambayar mai cewa; tun da akwai Kur'ani da sunnar Annabi (s.a.w) wane bukata kuma ake da ita ga Imami kamar yadda Shi’a suke imani da hakan?
Halifanci Bayan Wafatin Annabi

Halifanci Bayan Wafatin Annabi

Amma hadisai, cikinsu akwai: “Matsayinka a wajena irin matsayin Haruna wajen Musa ne sai dai ni ba Annabi Abayana”( ). “Kai macibincin duk wani mumini ne a bayana”( ). “Kur’ani na tare da Aliyu ba za su rabu ba har sai zo min a tafkin Alkausara”( ).
Halayen Imam Hasan (S)

Halayen Imam Hasan (S)

Imam Hasan (a.s) ya amsa wa sarkin mas'alolin da ya kawo zuwa ga babansa Imam Ali (a.s) domin a amsa masa su, sai Imam Ali (a.s) ya nemi dan sakon ya zabi wani daga 'ya'yansa domin ya amsa masa, sai ya zabi Imam Hasan (a.s).
Halayen Imam Ali (a.s)

Halayen Imam Ali (a.s)

Imam Ali (a.s) ya yaki kuraishawa suna kafirai, kuma ya yake su suna munafukai, kamar yadda ma'aikin Allah (s.a.w) ya yi masa alkawarin hakan. Game da tafiyar da dukiya kuwa ya yi wa musulmi jagoranci ne irin na lokacin manzon Allah (s.a.w), ya kasance yana cewa: "Da dukiyar nan tawa ce da na daidaita tsakaninsu, yaya kuwa, alhalin wannan dukiya ta Allah ce, kuma bayar da dukiya ba bisa hakkinsa ba barna ne, kuma yana daukaka mai yin haka a duniya, kuma ya kaskantar da shi a lahira, ya girmama shi gun mutane, ya kaskantar da shi gun Allah. Don haka ne ya yi kokarin samar da al'ummar da masu hannu da shuni ba su mamaye arzikin kasa ba, kuma ba a samu danniyar gurguzu ba.
Yankin Larabawa Kafin Annabi

Yankin Larabawa Kafin Annabi

“Hakika wannan kur’ani yana ambaton lokacin zamanin larabawa da yake tukewa har zuwa bayyyanar musulunci a lokacin jahiliyya, ba komai ba ne sai nuni daga gareshi zuwa cewa; abinda yake hukunci a cikinsu a wannan zamani shi ne jahilci ba ilimi ba, kuma abin da ya mamaye su a cikin kowane al’amari nasu ba komai ba ne sai barna ba gaskiya ba[5], sun kasance a kan hakan kamar yadda kur’ani ya ke ba mu labarinsu yana mai cewa: “Suna tsammani ga Allah abin da yake ba gaskiya ba zato na jahiliyya suna masu cewa shin mu na da wani makami na wani abu”. Ali imran: 154.
1 2 3 4 5 6 7 8 9