Karanta Kur'ani da Koyonsa

Karanta Kur'ani da Koyonsa

Daga Muhammad dan Fudail daga Abul Hasan (a.s) ya ce: "Na tambaye shi: ina karanta Kur'ani sai fitsari ya kama ni sai in tashi in yi fitsari sannan in yi tsarki in wanke hannuna sannan sai in koma wa littafi sai in karanta shi? Sai ya ce: A'a, har sai ka yi alwalar salla". Daga littafin Hisal da sanadinsa daga Ali dan Abu Dalib (a.s) a wani hadisi guda dari hudu ya ce: bawa ba ya karanta Kur'ani idan ya kasance ba bisa tsarki ba har sai ya yi tsarki" .
Mene ne kur’ani

Mene ne kur’ani

Kur’ani a lugga yana nufin karatu, Allah (s.w.t) yana cewa; “Idan muka karanta shi sai ka bi karatunsa”. Kur’ani; shi zance ne kuma littafi na Allah mai gajiyarwa ga wani ya zo da shi da Allah ya saukar da shi wahayi ga annabi (s.a.w) ta hannun Jibril (a.s) wanda aka rubuta a littafin mus’haf, da ya tabbata ta hanyar labarai mutawatirai wadanda ba yadda za a yi su zama karya, wanda kuma aka sanya karanta shi bauta ne ga Allah”.
1 2 3 4