bayyinaat

Published time: 13 ,July ,2018      22:32:15
Kawo gyara wani juzu'I ne da bai yiwuwa a cireshi daga gundarin harkar ilimi da imam sadik (as) ya mike kanta.
Lambar Labari: 164


Usulubi na biyu:
Yunkurin kawo gyara daga imam sadik (as) wannan fuskanta ta kawo gyara ta nau'antu a wajensa sai ya bugi kirji ya kalubalanci karkata daga kan shiriya ta wani bangaren kuma ya zamanto ya kasance yana kiyaye ingantacciyar fahimta ga addini karkashin iliminsa ta hanyar almajiransa da abin da ya bari daga munazarori da ilimummuka da aka dawana su aka rubuta da hadisan da aka rawaita daga gareshi (as)
Kawo gyara wani juzu'I ne da bai yiwuwa a cireshi daga gundarin harkar ilimi da imam sadik (as) ya mike kanta.
Hakika ya kalubalanci zindikai da gullatu da makaryata da masu da'awar imamanci da kawarijawa da mu'utazilawa da murji'a da wadanda suka tafi kan tanasuk (ruhin mamaci ya dawo jikin rayayye) da masu jikkanta Allah da suranta shi da `yan jabariya da mufawwida wanda suka tafi kan halittar kur'ani da wasunsu….

Kwadaitarwa kan kubutar da al'umma da kiyaye lafiyarta:
Sahabban imam sadik (as) sun banbanta da wasunsu da matakai da matsayai na jarumtaka da riko kimomi da ababen koyi madaukaka da rashin yaudara da rashin karkata ga kwadaitarwar sarakuna, sai ya zamanto sun jurewa wahalhalu da matsi da takurawa sakamakon lazimtarsu ga kyawawa halaye ababen koyi, matsayansu na jarumta sun sanya wani tasiri mai girman gaske cikin tabbatuwar gwagwarmaya al'ummar musulmi gaban guguwar bata da karkata.
Imam sadik (as) ya kasance yana neman dukkanin shi'arsa su kasance ababen koyi da madaukakan misalai cikin al'ummar da suke rayuwa cikinsu. Ya kuma kasance yana umartar shi'arsa da himmatuwa kan hadin kan musulmai da budewar kirji ga ragowar mazhabobi da karfafa ruhin rayuwa tare da juna da nuna kauna da karfafa hadewar jama'ar musulmai sai kaga mun same shi ya na kwadaitar da su zuwa ga haduwa da juna da cudanya da taimamkekeniya da juna da cika alkawari tare da ragowar muuslmai.

قال×: « عليكم بالصلاة في المساجد وحسن الجوار للناس وإقامة الشهادة وحضور الجنائز، إنّه لا بدّ لكم من الناس، إنّ أحداً لا يستغني عن الناس في حياته، والناس لابدّ لبعضهم من بعض »

Na umarceku da yin sallah cikin masallatai da kyawunta makotaka da tsayar da shaida da halartar jana'iza. Tabbas yadda al'amarin yake shi ne dole ne ku zauna tare da mutane lallai wani mutum bai wadatuwa ga barin ragowar mutane cikin rayuwarsa, su mutane dole ne sashensu yana bukatuwa zuwa ga sashe.
Imam (as) ya kasance yana yin dukkanin bakin kokarinsa wajen fuskantar da mutane da daidaita halayensu da gyara al'amuransu gwargwadon ikonsa, yana kuma nufinsu da su lazimtu da gundari su yi watsi da abin da ke bijirowa, yana umartarsu da yin aiki yana kiran masu wadata da ciyar da mabukata domin wanda ke cikin kuntata daga cikinsu ya yalwatu hakan kuma ya sanya su kamewa daga yin roko da bara shi da kansa imam (as) ya kasance yana ciyar da dukiyarsa har sai da ya kasance babu abinda ya yi ragowa hannunsa da zai ciyar da iyalinsa.  
Kamar yadda ya tsaya kyam kan kishiyantar masu yunkurin batawa muslunci suna da suke kokarin rusa shari'a da bijirar da ita zuwa ga karktarsu da bata ta hanyar shigar da bakin tunanunnuka kamar yadda ya kasance da sauran shari'o'I da suka gabata da amfani da sabbin hanyoyi domin fahimtar shari'a kamar misalin kiyasi da istihsan da msalihul mursala.
Sakamakon mustawar ilimi madaukakiya da sahabban imam sadik (as) da shi'arsa suke da shi kuma mas'alar yin fatawa kan maslahohin fadar sarakuna wadda take dacewa da maginarsu ta tunani da saye-saye ransu ba ta ma kasance garesu, bari dai fahimtar addini mai cin gashin kanta ta wanzu ta na nesanta daga amfani da wadancan hanyoyi baki kirkirarru da aka shigar da su cikin shari'a, lokaicin da wadancan mutane daban sukai amfani da wadancan hanyoyi na ijtihadi sai wannan tsageranci ya tuke ga haifar kufaifayi masu cutarwa wanda ya tilasta rufe kofar ijtihadi, wannan shawara ita tai kara haifar da sakamakon mara kyau ga al'ummar musulmi saboda rashin ikonsu ga warware cigaba sabo da yake zuwa da suke fuskantarsa kowacce rana a kasashen musulmai bayan wancan rufe kofar ijtihadin da sukayi.
Hakika imam sadik (as) ya karfafi wannan kaziyya mai matukar muhimmanci ya yi la'akari da ita wani jigo muhimmi cikin fahimtar addini ya kuma bayyanata da kuma yin istinbadi daga gareta wannan kaziyya bawani ba ce face malakar tak`wa (tsoron Allah) da adalci da ya zama lazimi a same su tare da fakihi domin ya kasance mai gadi aminatacce ga shari'a da al'umma da suke son dabbaka shari'a cikin rayuwarsu.
Imam (as) ya kasance yana ganin larurar aiki domin samar tsari na muslunci da ake bukatarsa hakan na tabbatuwa ta hanyar samar da jama'a musulmai nagargaru salihai wadanda sukai imamni da jagorancin shari'a ta hakika wacce take misalantuwa cikin a'imma ahlul-baiti (as)
Haka imam (as) ya kasance yana janyo hankula zuwa ga larurar samar wannan ingantacciyar ka'idar lokacin da ya kasance yana amsa tambayoyi da suke kai kawo cikin zukatan sahabbansa kamar misalin jawabin a ya baiwa sudairur sairafi yadda ya kasance ya zo cikinsa cewa tabbas neman kafa hukuma da shelanta juyin-juya hali wanda ke dauke da makami ya dogara da samun mutane salihai masu biyayya da sadaukar da kai da daukar nauyin samar da canji dole kuma ya kasance suna kudura kan fuskantar dukkanin harkokin bata da karkata.
Hakika imam (as) ya yi kai kawo wajen karfafa wayewar jihadi cikin wadannan mutane salihai karkashin natijojin saura husainiya ta yadda wannan saura wanzazziya mai albarka ta kimsa kalubalantar  batattun shuwagabanni karkatattu, al'ummar musulmai albarakicin wannan saura sun samu damar ketare yaudarar umayyawa da suka kirkira domin bawa kansu halascin mulki, wannan wayewa na juyin-juya hali da aiki na jihadi wanda al'umma ta samar cikin tsawon shekaru na iya faduwa kasa banza idan ya kasance ba a cudanya ta da dalilan da zu wanzar da ita ba da kammala ta.
Wannan na bayyana a sarari karkashin matsayarsa kan saurar baffansa zaidu ibn ali (as) ta yanda ya bayani karara yana mai cewa:  
   
«أَشْرَكَني الله في تلك الدماء. مضى والله زيد عمّي وأصحابه شهداء مثل ما مضى عليه علي بن أبي طالب وأصحابه »

Allah ya yi tarayya dani cikin wadancan jinane,wallahi baffana Zaidu da sahabbansa sun tafi suna shahidai kamar yadda aliyu ibn abi dalib (as) da sahabbansa suka tafi.
Wannan matsaya daga gareshi (as) yana bada halasci ga saurar Zaidu yan kuma ayyanawa jama’a salihai buri da fatan imam (as) ya na kuma sanya su rayuwa da himmatuwa kan jihadi da juyi wanda imam (as) ke nufinsa ga wasu jama’a nagargaru da zasu iya tafiya zuwa ga fuskanin haduffa da ake bukata ga jagorancin ubangiji da ke misaltuwa cikin imam sadik (as)
Jama’a salihai suna samfuri na musammam wanda imam ya tanade shi don kawo gyara cikin al’ummar musulmi.
Daga cikin uslubansa da wannan kebantaccen al’amari shi ne karfafarsa kan jumlar wasu hanyoyi misalin ziyara da raya majalisan husainiyya da kuka.
imam sadik (as) ya yi la’akari da ziyarar kabarin kakansa imam husaini (as) matsayin wani hakkin na lazimi wacce ya zma wajibi kan dukkanin musulmi himmatuwa da ita wacce ya zama wajibi a sauke nauyinta

قال×: « لو أن أحدكم حجّ دهره ثم لم يزر الحسين بن علي× لكان تاركاً حقّاً من حقوق رسوله: لأنّ حقّ الحسين× فريضة من الله عزّوجلّ واجبة على كل مسلم».

Ya ce: da ace dayanku zai je aikin hajji tsawon zamaninsa sannan ace ya bar ziyartar husaini da ya kasance daga wadanda suka bar hakki daga hakkokin manzon Allah (s.a.w) saboda hakkin husaini (as) farilla ce daga Allah mai girma da daukaka wajibi ce kan dukkanin musulmi.
 
وقال×: « من سرّه أن يكون على موائد النور يوم القيامة فليكن من زوّار الحسين بن علي×».

Ya ce: wanda ya faranta masa ace ya kasance kan teburan walimamr haske ranar kiyama to ya kasance daga maziyartan husaini ibn ali (as)

daga cikin matakai da imam sadik (as) ya fara motsawa karkashinta ita kaziyyar juya yi da jimamin shahadar imam husaini (as) hakika imam ya karfafata ya dauketa matsayin wani uslubi daga usluban tarbiyya da motsa soyayya da kuna domin alakanta al’umma da saurar imam husaini (as) ya kasance yana shirya wadannan majalisai na jimami a kebance domin cimma wancan manufa.

قال× لأبي هارون المكفوف: «يا أبا هارون أنشدني في الحسين × قال فأنشدته، فبكى.
ثم قال: زِدني، قال: فأنشدته القصيدة الأخرى، قال: فبكى وسمعت البكاء من خلف الستر. قال: فلمّا فرغت قال لي: «يا أبا هارون من أنشد في الحسين× شعراً فبكى وأبكى عشراً كتبت له الجنّة، ومن أنشد في الحسين× شعراً فبكى وأبكى خمسة كتبت له الجنّة، ومن أنشد في الحسين× شعراً فبكى وأبكى واحداً كتبت له الجنّة»

Imam sadik (as) ya cewa abu haruna makfuf: ya abu haruna raira mini waka cikin husaini (as) sai na raira masa wakar ya yi kuka, sannan ya ce: kara rerawa, sai na kara raira masa wata kasidar sai ya yi kuka sai naji sautin kuka daga bayan labule. Ya ce: ya yinda da na gama rairawa sai imam ya ce mini: ya abu haruna duk wanda ya raira waka cikin husaini (as) ya yi kuka ya kuma sanya mutane biyar kuka an rubuta masa aljanna, duk wanda ya raira waka cikin husaini (as) ya yi kuka ya sanya mutum guda kuka an rubuta masa aljanna.


: «يا فضيل تجلسون وتتحدّثون ؟ قلت: نعم سيدي قال: «يا فضيل هذه المجالس أحبّها، أحْيُوا أمرنا. رحم الله امرءاً أحيا
 أمرنا
Imam (as) ya kasance yana karfafa raya tunawa da imam husaini (as) kamar yadda muka ga hakan cikin fadinsa ga fudailu: (ya fudailu shin kuna zama kuna zantar da hadisinmu? sai nace masa na’am ya shugabana ya ce: ina son wannan majalisai, ku raya al’amarinmu. Allah ya jikan mutum da ya raya al’amarinmu)
Hakika ya zo daga imam (as)
   
« إن البكاء والجزع مكروه للعبد في كلّ ما جزع ما خلا البكاء والجزع على الحسين بن علي× فإنّه فيه مأجور.

Lallai kuka da raki makaruhi ne ga bawa cikin komai sai dai kuka da raki cikin husaini (as) tabbas cikinsa akwai lada.

A mustawan ruhi al'umma a zamanin imam sadik (as) sun bijira zuwa ga raunana da yaushi do nuna son kai sakamakon kungiyoyin d suke samun tallafi daga fadar sarakunan banu umayya da banul abbas kishiyar haka imam sadik (as) ya tashi da samar da jumlar wasu ayyuka wadanda suke `daga imamnin al'umma daga cikin wadannan ayyuka akwai:
Gargadin imam daga kulla alakar imamni tare da wadanda suke kiran kawukansu da malamai da kuma hana karkata da koyi da su, tabbas wannan yana daga nau'in alakar da take bata alaka da Allah ya ce:
«أوحى الله إلى داود×: لا تجعل بيني وبينك عالماً مفتوناً بالدنيا فيصدّك عن طريق محبّتي : فإنّ أولئك قطّاع طريق عبادي المريدين، إنّ أدنى ما أنا صانع بهم أن أنزع حلاوة مناجاتي من قلوبهم»

Allah ya yi wahayi zuwa ga dauda (as): ka da ka sanya wani malami da ya fitinu da duniya tsakanina da kai zai koreka daga hanyar soyayya ta: tabbas wadancananka sune barayin kan hanyar bayina masu nufi, tabbas mafi kusa abin da na keyi da su shi ne in cire musu zakin munajati da ni daga cikin zukatansu.

comments Masu kallo
Suna:
Adireshin Email:
* ra'ayi: