bayyinaat

Al umma
Mace Musulma
Wadannan dukkaninsu sun tafi akan halarcin auren mtutu'a suna masu dogara da wannan ayar, har wasunsu ma sun kara kalmar "zuwa wani lokaci" a gaban wannan ayar kamar haka:
A shar'ance Auren Mutu'a yana da sunaye da aka san shi da su, ana kiran sa "Aure Mai Iyaka" ko "Auren Jin Dadi", "Aure Mai Ajali".
Sukan Auren Mace Fiye Da Daya
Auren mace fiye da daya zuwa hudu yana karya zuciyar mata sai su daina aikin gida, su nemi daukar fansa da kin kula da tarbiiyar yara, kai suna iya neman wasu maza sai su shiga ha’inci, zina, fasikanci, da barnar dukiya. 2-Auren mata hudu ya saba wa dabi’ar halitta domin ta tanadar wa kowane namiji mace daya ne shi ya sa yawansu yake kusan daidaita. 3-Auren mace fiye da daya zai kwadaitar da maza bin shwa’awa da zari, da son zuciya. 4-Auren mace fiye da daya ya saba wa shi kansa musulunci domin an ce: Namiji yana da ninki daya ne kan mace a gado da shaida da sauransu, me ya sa a aure har hudu ba biyu ba?
Auren Mace Fiye Da Daya
Allah madaukaki yana cewa: “Kuma idan kuka ji tsoron ba zaku yi adalci ba a game da marayu, to sai ku auri abin da ya yi muku dadi daga mata, biyu-biyu, uku-uku, da hudu-hudu, amma idan kuka ji tsoron ba zaku yi adalci ba, to (ku auri mace) daya ko abin da hannayenku suka mallaka…” .
Marhalolin Tarihin Mace
Tarihin rayuwar mace yana cike da duhu a cikin al'ummu sakamakon danniya da ta fuskanta a cikinsu, sakamakon haka ne Allah madaukaki ya aiko da 'yan sako a cikin lokuta da marhaloli da zamuna mabambanta, zuwa ga al'ummun nahiyoyin wannan duniyar domin su fitar da su daga wannan duhun zuwa ga haske. Sai dai a ko da yaushe suka juya baya sai al'ummu su sake koma wa cikin al'adunsu, su dulmuya cikin duhunsu, su ci gaba da fandare wa ubangijinsu.