Littafin Buhari da Muslim a Ma'auni yana bahasi ne kan ruwayoyi da suka shafi annabin rahama (s.a.w) da yadda aka cusa su a ruwayoyin musulmi alhalin sun saba wa koyarwar addini mai inganci da ta zo a cikin littafin Allah madaukaki da ya tsarkake annabinsa mai daraja da daukaka. An bi kowane fasali da ya yi maganar wani abu wanda ya saba wa Kur'ani game da siffofin annabin daraja da kamala domin tsarkake shi daga duk wata dauda da aka jingina masa amincin Allah ya tabbata gare shi.
Lambar Labari: 60
comments Masu kallo