bayyinaat

Sīrāh
Annabin Daraja
Rayuwar Annabi Muhammad
An ambaci shekarar haihuwarsa da “Shekarar giwa”[1], saboda harin da Habasha ta kai wa Ka’aba domin rusa ta a wannan shekarar. Kuma abubwan mu’ujiza sun wakana yayin haihuwarsa (s.a.w) da suka hada da: 1-Faduwar gumaka akan fusakunsu. 2-Rushewar katangun kisira da suke Shiraz. 3-Mutuwar wutarsu da suke bautawa. 4-Kafewar kogin Sawa. 5-Dukkan wadannan abubuwa sun faru ne a shekarar miladiya ta 571 ne[2].
Yankin Larabawa Kafin Annabi
“Hakika wannan kur’ani yana ambaton lokacin zamanin larabawa da yake tukewa har zuwa bayyyanar musulunci a lokacin jahiliyya, ba komai ba ne sai nuni daga gareshi zuwa cewa; abinda yake hukunci a cikinsu a wannan zamani shi ne jahilci ba ilimi ba, kuma abin da ya mamaye su a cikin kowane al’amari nasu ba komai ba ne sai barna ba gaskiya ba[5], sun kasance a kan hakan kamar yadda kur’ani ya ke ba mu labarinsu yana mai cewa: “Suna tsammani ga Allah abin da yake ba gaskiya ba zato na jahiliyya suna masu cewa shin mu na da wani makami na wani abu”. Ali imran: 154.
Halayen Manzon Allah (s.a.w)
Ya zo a babin ci da shan manzon Allah (s.a.w) cewa: "Manzon Allah (s.a.w) ya kasance yana cin dukkan nau'o'in abinci, tare da iyalansa da masu yi masa hidima, kuma yana ci tare da wadanda ya kira su na musulmi a kasa, kuma a kan abin da suka ci da kuma daga abin da suka ci, sai dai idan bako ya zo masa to sai ya ci tare da bakonsa".
Halayen Manzon Allah (s.a.w)
Domin samun tsira dole ne mutum ya kasance yana da akida sahihiya, da biyayya ga umarnin Allah da manzonsa da suke kunshe cikin littafin Allah da sunnar manzonsa, da kuma bibiyar kyawawan halaye manzon rahama Muhamamd dan Abdullah (s.a.w) da wasiyyansa tsarkaka da suka kama tun daga Imam Ali har zuwa Imam Mahadi (a.s). Don haka babu wani wanda ya fi dacewa a yi nuni da halayensa don a yi koyi da shi sai wannan gida da Allah bai yi kamarsa ba.
2