Akida
Kadaitaka
Muna ganin ni’imomin halitta da suka babaye mu, ni’imar rana, da ni’imar dare da ba mu san iyakacin su ba, ni’imar iska, da ruwa, da lafiya, da tunani, da zafi, da sanyi, da shiriya, ta hankali da ta wahayi, da sauran ni’imomi da ba zasu kirgu ba.
Domin da ya kasance kamarta ne, da ya bukaci mai samarwa, don haka dole a tuke zuwa ga mai samarwar da ba samar da shi aka yi ba, wanda yake shi ne ainihin samuwa.
Wajibi ne a kan baligi ya san Allah madaukaki, bai halatta ba ya bi wani a kan haka ba koda kuwa babansa ne, misali dole ya yarda Allah daya ne, ta yadda da babansa ko malaminsa zai ce Allah sabanin haka ne, to ba zai bi ba.